Thursday, January 10, 2008

Gamji Dan K'warai

Gamji Dan Kwarai, Allah yayi masa Rahama Amin. A 15-01-2008 yake cika shekaru 42 da kwanta dama, kuma har yanzu yana nan a zukatan Y'an Nijeriya, ba'a manta dashi ba, Anamasa Addu'a, Allah yajikan mazan K'warai. To wai Meyasa wanda suke raye ba'a ambatansu? se matattu kuma tun ayyukan dasukayi wa kasa duk tsawon wannan shekarun, har yanzu ana amfana dasu, irinsu Jami'ar Ahmadu Bello da sauransu, ina shugabannin mu wanda su Sardauna suka rena? Ina Yan k'asa na kwarai? shin kuna tsammanin a bayan ranku za'a tuna daku? Yakamata ku sake tunani kusan irin abinda zaku aikatawa Al'ummarku tun kafin Ajali yazo maku ayimaku Addu'a ba'a la'aceku ba, Sarakuna ku dauki tafarki da Sardauna yabi domin Martabar ku ta dawo a Idanun jama'a, ba wai kutaru a gidan Sardauna, ba kuyi jawabai shike nan, a watse A'a kuyi abinda ze daukaka Al'ummar mu, dare beyiba ga duk wanda yake darai kowa yayi da kyau zega da kyau Allah ya jikansu Ahmadu Bello Amin.

No comments: