Sunday, March 9, 2008

ABIN KUNYA DA KO DABBA TAKE KYAMATA

Wani abin mamaki ne naci karo dashi wanda hankali baze taba tunanin yiwuwan aukuwan hakan ba, sannan koyaya mutum yakai da rashin kishi da lalacewa ze la'ance wannan danyen aikin, bugu da kari hakan yasa wasu yan iska marasa kima da sanin mutuncin addini suke batanci ga Manzan Allah Sallallahu Alaihi wasallam, da cewa wai shi ya karantar da aikata wannann mummunana aikin , wani dabban kuma daga kudu hakan tasa yake zagi ga al'adunmu da sarakunanmu cewa irin abubuwan da suke aikatawa kenan aboye kai abinda yafi muni ma shine ta'alikin da wani musulmi me suna Alhaji yayi na nadamam kasancewarsa musulmi saboda karanta wannan labarin. Allah ya kiyaye! To koma me zasu fada nidai yayin da na karanta wannan labari hankali na ya tashi da yin tunanin shin yanzu akwai wani mahalukin daze aikata hakan kuma musulmi a garin musulmi kai a garin da akema aiwatar da Shariar musulunci? to wane irin danyen aikine kuwa ya haifar da abubuwan da muka ambata? Shine Labarin Auwalu Muhammad mazaunin Unguwar Yakasai a cikin birnin Kano wannan aka gabatar dashi a gaban kotu wanda me sharia Maryam Ahmad Sabo ta jagoranta, shi da yayansa biyu Hadiza Yar shekara sha hudu, da kanwanta Nana Aisha yar shekara sha biyu, wanda mahaifiyarsu tayi yaaji saboda Uban wato Auwalu yana kwana dasu bayan ta hanashi yaki dena aikata hakan, ita Hadiza Yanzu haka tana dauke da cikin wata tara, - Allah yakiyaye Yarka matarka Jikanka yarka ko danka- ta bayyana ma koyu cewa sun tafi wajen yan uwansu amma uban yadawo dasu yana ya maidasu kaman matansa, kuma Shedanin Uban ko a jikinsa yana fita harkar kasuwancinsa seda aka kaishi kara be ko damuba, Allah ya shiryamu dashi gaba daya Amin. Daga jaridar Weekly trust 08/03/2008 me rahoto jaafar jaafar kano. To mudai mun kasa kunne muna jira muji hukuncin kotu. Saboda munsan hukuncin wanda yayi lalata da muharramansa shine kisa a shariar musulunci. Allah ya shirya mu Amin

No comments: